Bakonmu A Yau

Informações:

Sinopsis

A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.

Episodios

  • Abba Terab kan cire tallafin lantarki a Najeriya

    05/04/2024 Duración: 03min

    Hukumar Kula da wutar lantarki a Najeriya ta sanar da cire tallafin da gwamnati ke zubawa a bangaren samar da wutar ga wasu mutane, abinda ya shafi farashin wutar. Tuni jama’a da kungiyoyin kwadago da kuma masu masana’antu suka bara dangane da matakin da kuma abinda suka kira illar dake iya biyo baya.Malam Abba Terab, babban jami’i a hukumar ya yiwa Bashir Ibrahim Idris bayanin matakin da aka dauka a tattaunawar da suka yi a kai.Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.

  • Dr Abdullahi Gwandu kan fara fitar da tatatcen mai, na matar man Dangote

    04/04/2024 Duración: 03min

    Matatar man hamshakin attajirin Najeriya Aliko Dangote ta fara fitar da albarkatun man fetur din da ta tace, kamar yadda daya daga cikin manyan jami’an kula da matatar da kuma kungiyar dillalan man fetur din a Najeriya suka tabbatar. A cewar jami’in, ya ce tuni suka fara rarraba wa ‘yan kasuwa man disel da kuma man jiragen sama, inda kuma ya ce litar mai miliyan 37 suke fatan cimma fara dorawa manyan jiragen ruwa, amma a halin yanzu suna iya lodin litar man miliyan 26. Ko wannan mataki zai kawo karshen shigar da tatatcen mai cikin Najeriya ke nan? Kan haka ne Khamis Saleh ya zanta da Dr Abdullahi Abubakar Gwandu, na kwalejin kimiya da fasaha ta kasa da ke Kaduna.Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar zantawar tasu.......

  • Dr Kasim Garba Kurfi kan matakin CBN na kara yawan jarin bankunan kasar

    03/04/2024 Duración: 03min

    Babban Bankin Najeriya ya bai wa bankunan kasuwancin kasar umarnin kara yawan jarin su domin tafiya da zamani, wanda ya kunshi jarin naira biliyan 50 ga bankunan shiya da kuma naira biliyan 500 ga bankunan da ke hada hada da kasashen ketare. Domin sanin tasirin wannan mataki, Abdulkadir Haladu Kiyawa ya tattauna da masanin tattalin arziki, Dr Kasum Garba Kurfi. Ku latsa alamar sauti don jin yadda zantawar su ta gudana.........

  • Comrade Bashir Dauda kan halin tsaro da ake ciki a jihar Katsina

    02/04/2024 Duración: 03min

    Jihar Katsina da ke Najeriya na daya daga cikin jihohin da ke fama da matsalar 'yan bindiga a yankin Arewa maso Yammacin kasar. Duk kokarin hukumomi jihar na sasantawa da 'yan bindigar yaci tura. Dangane da halin da jihar ke ciki kan matsalolin tsaro, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Comrade Bashir Dauda sakataren kungiyar muryar talata a Najeriya.Ku latsa alamar sauti don jin cikakken zantawar tasu.....

página 2 de 2